fidelitybank

NDLEA ta kama mutanen da take nema ruwa a jallo

Date:

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya NDLEA ta kama wasu mutane da ta shafe wata biyu tana farautarsu bayan da ta zarge su da ƙwarewa wajen safarar miyagun ƙwayoyi tsakanin Najeriya da Afirka ta Kudu da Mozambique da ƙasashen Turai da Amurka.

Cikin wata sanarwa da hukumar ke fitarwa mako-mako, da mai magana da yawun hukumar Femi Babafemi ya aike wa da BBC ya ce hukumar ta kama mutanen ne bayan kama wata hodar ibilis mai yawa a filin jirgin sama na Legas.

Sanarwar ta ce hukumar samu nasarar kama biyu daga cikin mutanen da ta jima tana nema ruwa-a-jallo, watao Onyinyechi Irene Igbokwuputa da kuma Frankline Uzochukwu ranar Juma’a 19 ga watan Afrilu a filayen jirgin saman Legas da na Awka.

Sai kuma Osita Emmanuel Obinna wanda ta kama shi a birnin Legas.

Hukumar ta NDLEA ta kuma ce takama wani mutum da ya yi yunƙurin fita da tabar wiwi da nauyinta ya kai kilogiram 9.80, daga Najeriya zuwa ƙasar Oman.

”Bayan hukumar ta kama shi ya bayyana cewa an ƙulla yarjejeniyar cewa za a biya shi naira miliyan 1,200,000 idan har ya fitar da tabar zuwa Oman”, in ji sanarwar.

Babafemin ya kuma ce a ranar 20 ga watan Afrilu hukumarsa ta kama wani direban mota a Girei kan hanyarsa ta zuwa Mubi, inda jami’an hukumar suka kama ƙwayar ‘opioids’ da ke sa maye da yawanta ya kai miliyan 1,250,000 mai nuyin kilogiram 450.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp