fidelitybank

NDLEA ta kama matasa 111 da safarar mugan kwayoyi a Kaduna

Date:

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta NDLEA ta jihar Kaduna ta bayyana cewa, ta kama mutane 111 masu safarar miyagun kwayoyi, tsakanin watan Janairu zuwa Fabrairun 2022 a jihar.

Kwamandan rundunar, Umar Adoro, ne ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN), ranar Alhamis, a Kaduna.

Ya ce, yawancin wadanda ake zargin sun kai shekaru 16 zuwa 30.

Ya bayyana cewa an kama mutane 34 a watan Janairu daga cikinsu 31 maza ne, yayin da uku kuma mata ne, ya kara da cewa an kuma kama kwayoyi masu nauyin kilogiram 295.680.

“Mun kama 292.125kg na Cannabis Sativa, 0.001kg na Heroin da 3.554kg na abubuwan da ke damun kwakwalwa kamar Benalin, tramadol da sauransu.

“A watan Fabrairu, mun kama mutane 77 da ake zargi daga cikinsu 74 maza ne yayin da uku kuma mata; kuma an kama jimillar kwayoyi 320.508,” inji shi.

Adoro ya bayyana cewa daga cikin adadin magungunan da aka kama 294.101kg sun hada da Cannabis Sativa, 0.034kg Cocaine, 0.005kg Heroin yayin da 26.358kg na psychotropics da 0.010kg Methamphetamine.

Ya kara da cewa, hukumar ta kuma gano wani sabon alkalami mai dandanon Shisha, wanda dandanonsa na dauke da man wiwi, wanda matasa ke amfani da shi.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp