fidelitybank

NDLEA ta kama Fasto kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Date:

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya, NDLEA, ta ce ta kama wani babban faston majami’ar The Turn of Mercy Church, Adefolusho Olasele, kan zarginsa da hannu a safarar miyagun ƙwayoyi daga Ghana zuwa Najeriya.

An kama Olasele ne wanda ya shafe tsawon watanni yana tserewa hukumomi a ranar Lahadi, 3 ga Agustan 2025 – a cocinsa da ke Okun Ajah, a jihar Legas.

Wata sanarwa da mai magana da yawun NDLEA, Femi Babafemi ya fitar, ya ce jami’an hukumar sun jira sai da faston ya gama wa’azinsa kafin daga bisani suka cafke shi lokacin da yake barin harabar cocin.

A cewar Babafemi, faston ya tsere zuwa Ghana a watan Yuni, bayan da jami’ai suka alaƙanta shi da wasu ganyen wiwi da aka kama mai nauyin kilogiram 200 a bakin ruwa na Okun Ajah ranar 4 ga watan Yuni da kuma wanda aka samu a cikin motarsa.

Babfemi ya ce malamin majami’ar ya amsa cewa yana safarar ƙwayoyi ta ruwa daga Ghana zuwa cikin Najeriya.

www.legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari a ƙauyuka 15 na Zamfara a mako ɗaya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...

A karon farko an gurfanar da Mutanen da ake zargi da kai hari Cocin Owo

Mutum biyar da ake zargi da shirya harin bam...

Peter Obi na nan a cikin jam’iyyar har yanzu – LP

Shugaban ƙungiyar Obidient Movement, Dr. Tanko Yunusa ya ce...

Yadda Mahara sun kashe mutum biyu, sun ƙona gidaje a Filato

Wasu da ake zargin mahara sun afka wa karamar...

An YI zanga-zanga a Isra’ila kan shirin Netanyahu na mamaye Gaza

Dubban mutane sun fito kan tituna a faɗin Isra'ila,...

Birtaniya za ta fara tisa ƙeyar bakin da suka aikata laifi zuwa kasarsu

Birtaniya ta fitar da sabon tsarin tisa keyar duk...

NDLEA ta kama Fasto kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Gwamnoni sun mika sakon ta’azziya ga iyalan Audu Ogbeh

Shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu...

Duk wahala sai dai mu mutu a Gaza – Fatma

Wata mai mai ƴaƴa tara ta ce, duk runtsi...

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...
X whatsapp