fidelitybank

NDLEA ta kama Fasinja da hodar Ibilis guda 80 a filin jirgin sama

Date:

Jami’an Hukumar da ke Hana sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya (NDLEA) ta cafke wani fasinja a filin jirgin sama na Murtala Muhammad da ke jihar Legas ɗauke da kullin hodar iblis guda 80.

An kama Ogbonna ne a ranar Lahadi, 31 ga Maris, 2024, a lokacin da yake yunkurin hawa jirgin Qatar Airways zuwa birnin Delhi na ƙasar Indiya, ɗauke da fasfo ɗin ƙasar Laberiya.

NDLEA ta bayyana kama mutumin ne a wata sanarwa da kakakinta Femi Babafemi ya fitar a ranar Lahadi.

Babafemi ya ce an yi wa wanda ake zargin gwaje-gwaje, inda aka gano cewa yana tu’amalli da miyagun kwayoyi.

“Mun yi mamaki da muka gano yawan kwayoyi da a haɗiye a cikinsa, nan da nan ya fara yin amai na kullin hodar iblis da ya haɗiye,” in ji Babafemi.

NDLEA ta ce mutumin da ake zargi ya yi iƙirarin cewa wani dan uwansa ne ya ɗauke shi aiki don ya rika safarar kwayoyi.

An kuma samu ɗaurin hodar iblis guda 80 mai nauyin kilogram 889 a wajensa wanda ya amayar cikin kwanaki huɗu.

“Abin da ya kusa janyo ya rasa rayuwarsa shi ne, Ogbonna ya ce an ba shi kwayoyi domin ya hadiye a wani otel a Ikeja, tare da yi masa alkawarin tukuicin Naira 300,000 idan ya yi nasarar kai hodar iblis din zuwa Indiya,” in ji sanarwar NDLEA.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp