fidelitybank

NDLEA ta kama fasfo din kasashen waje a cikin buhun Gari

Date:

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, ta kama fasfo din kasa da kasa guda 22 na kasashe shida daban-daban da aka boye a cikin buhun Gari da dai sauran kayayyakin abinci.

Jami’an tsaro sun kama su ne a filin jirgin sama na Murtala Muhammed International na Ikeja dake jihar Legas, a harabar tashar SAHCO da ke filin jirgin a lokacin da suke aikin binciken kayan da suka saba yi.

Mai magana da yawun hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadin, ya ce tara daga cikin fasfo din uku ne kowannen su na Birtaniya da Faransa da Portugal da na Najeriya 8 da Ghana 4 da kuma na Kamaru 1.

Ya kuma ce a filin jirgin, jami’an sun kwato fakiti 12 na tabar wiwi mai nauyin kilogiram 4.95 da aka boye a cikin kwalin Golden Morn da aka shirya domin fitar da su ta cikin rumbun ajiyar kayayyaki na SAHCO.

A halin da ake ciki, Babafemi ya bayyana cewa, a jihar Filato, tawagar jami’an NDLEA a ranar Juma’a 28 ga watan Janairu, sun kama wasu mutane biyu da ake zargi ciki akwai Emeka Ezenwa mai shekaru 37 da Julius Akingbe mai shekaru 45 da haihuwa, bisa laifin mallakar gram 126.5 na sinadarin methamphetamine da aka boye a cikin na’urar DVD da ta taho daga Legas.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ʙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar ʊangote wajen haʙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ā€˜Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Ę“an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Ę“an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe Ę“an...
X whatsapp