fidelitybank

NDLEA ta kama fasfo din kasashen waje a cikin buhun Gari

Date:

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, ta kama fasfo din kasa da kasa guda 22 na kasashe shida daban-daban da aka boye a cikin buhun Gari da dai sauran kayayyakin abinci.

Jami’an tsaro sun kama su ne a filin jirgin sama na Murtala Muhammed International na Ikeja dake jihar Legas, a harabar tashar SAHCO da ke filin jirgin a lokacin da suke aikin binciken kayan da suka saba yi.

Mai magana da yawun hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadin, ya ce tara daga cikin fasfo din uku ne kowannen su na Birtaniya da Faransa da Portugal da na Najeriya 8 da Ghana 4 da kuma na Kamaru 1.

Ya kuma ce a filin jirgin, jami’an sun kwato fakiti 12 na tabar wiwi mai nauyin kilogiram 4.95 da aka boye a cikin kwalin Golden Morn da aka shirya domin fitar da su ta cikin rumbun ajiyar kayayyaki na SAHCO.

A halin da ake ciki, Babafemi ya bayyana cewa, a jihar Filato, tawagar jami’an NDLEA a ranar Juma’a 28 ga watan Janairu, sun kama wasu mutane biyu da ake zargi ciki akwai Emeka Ezenwa mai shekaru 37 da Julius Akingbe mai shekaru 45 da haihuwa, bisa laifin mallakar gram 126.5 na sinadarin methamphetamine da aka boye a cikin na’urar DVD da ta taho daga Legas.

hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ʙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

ʘungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Ę“an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ʓanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ʙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buʙaci gwamnonin ʙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp