fidelitybank

NDLEA ta ja hankalin matafiya a kan sabon salon damfara

Date:

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta NDLEA ta ja hankalin al’umma musamman matafiya zuwa ƙasashen waje kan sabuwar hanyar zambar da ake yi da sunan jami’an hukumarsu.

Kakakin hukumar Femi Babafemi ne ya sanar da hakan a ranar Asabar a Abuja, yana cewa masu zambar suna kira iyalan matafiya suna kiran ‘yan uwansu suce sun kama su a filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas ko kuma wani filin jirgin su ce an kama su da kwayoyi yayin saukarsu.

“Bayan jefa iyalan cikin firgici sai masu zambar su sake kiran ‘yan uwan mutanen su nemi a biya su miliyoyin nairori domin ganin yadda za a yi a saki wanda aka kama da yanzu ake tsare da shi a hannun NDLEA,” in ji Femi.

“Mun daƙile irin wadannan laifuka a bya, wani lokacin iyalan ke kiran jami’anmu domin neman tabbaci kan lamarin.”

Sannan kuma ya musanta hannun jami’ansu cikin abin da ya faru a bayan nan, inda aka ji muryar wani mutum da ya ce shi jami’in NDLEA ne yana tattauna yadda wata mata za ta biya naira miliyan biyar domin sakin wani mutum da ya zo daga Amurka da ya ce sun kama shi a filin jirgin MMIA da ke Legas a ranar 22 ga watan Maris, kuma an same shi da kwayoyi.

Daga baya aka shawarce su ka da su biya kuɗin da aka nema.

Femi ya shawarci al’umma su kiyayi tattaunawa da iyalansu kan tafiyar da ke gabansu, somin kaucewa irin wannan zambar da maha’intar ne ke shiryawa.

Ya kuma bayar da lambar wayar hukumarsu ga duk mutumin da ya samu kansa a irin wannan yanayi ya yi maza ya shaida musu +2347064670026 and +2348033326327.

bbc nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp