fidelitybank

NDLEA ta gana da hukumomin Pakistan a kan dakile safarar kwayoyi

Date:

Hukumar Hana sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta NDLE, ta ce, ta gana da hukumomin ƙasar Pakistan, domin gano hanyoyin da za a magance matsalar safarar ƙwayoyi tsakanin ƙasashen biyu.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukuma femi Babafemi ya fitar ƙarshen mako ya ce shugaban hukumar Bugediya janar Buba Marwa mai ritaya ne ya tura tawagar jami’an domin tattaunawar wadda ta gudana a birnin Vienna na ƙasar Austria.

”Tattaunawar da ƙasashen biyu kan safarar ƙwayoyin tsakanin ƙasahen biyu ta gudana ƙarƙashin jagorancin hukumar safarar ƙwayoyi ta duniya, ta kuma mayar da hankali ne wajen inganta harkokin sadarwa tare da musayar bayanan sirri tsakanin NDLEA da kuma hukumar hana sha da fataucin ƙwayoyi ta Pakistan’’ kamar yadda sanarwar ta bayyana.

A ƙarshen ganawar ƙasashen biyu sun cimma matsaya kan yadda za su inganta haɗin gwiwa wajen magance matsalar safarar miyagun ƙwayoyi musamman ƙwayar Tramadol tsakanin ƙasashen biyu.

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp