fidelitybank

NDLEA ta gana da hukumomin Pakistan a kan dakile safarar kwayoyi

Date:

Hukumar Hana sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta NDLE, ta ce, ta gana da hukumomin ƙasar Pakistan, domin gano hanyoyin da za a magance matsalar safarar ƙwayoyi tsakanin ƙasashen biyu.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukuma femi Babafemi ya fitar ƙarshen mako ya ce shugaban hukumar Bugediya janar Buba Marwa mai ritaya ne ya tura tawagar jami’an domin tattaunawar wadda ta gudana a birnin Vienna na ƙasar Austria.

”Tattaunawar da ƙasashen biyu kan safarar ƙwayoyin tsakanin ƙasahen biyu ta gudana ƙarƙashin jagorancin hukumar safarar ƙwayoyi ta duniya, ta kuma mayar da hankali ne wajen inganta harkokin sadarwa tare da musayar bayanan sirri tsakanin NDLEA da kuma hukumar hana sha da fataucin ƙwayoyi ta Pakistan’’ kamar yadda sanarwar ta bayyana.

A ƙarshen ganawar ƙasashen biyu sun cimma matsaya kan yadda za su inganta haɗin gwiwa wajen magance matsalar safarar miyagun ƙwayoyi musamman ƙwayar Tramadol tsakanin ƙasashen biyu.

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp