fidelitybank

NDLEA ta cafke kwayoyin da aka shigo da su daga Brazil da Canada

Date:

Hukumar da ke Hana Sha da Fataucin miyagun kwayoyi NDLEA, ta ce ta samu nasarar kama hodar ibilis da tabar wiwi da aka shiga ƙasar da ita daga ƙasashen Brazil da Canada a a biranen Enugu da Legas.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Femi Babafemi ya sanya wa hannu, ta ce hukumar ta kama ƙwayoyin tramadol miliyan 1.7 a birnin Legas da ke kudu maso yammacin ƙasar, tare da kama mutanen da ta daɗe tana nema a jihohin Osun da Kano da Ondo da Edo da Abuja babban birnin ƙasar.

Sanarwar ta ci gaba da cewa ”Jami’an hukumar NDLEA da ke aiki a filin jirgin saman Akanu Ibiam da ke Enugu da masu aiki a tashar jirgin ruwa na Tican da ke Legas sun samu nasarar daƙile yunƙurin shigo da kilogiram 126.95 na hodar ibilis da tabar wiwi ƙunshe cikin ƙwalayen ganyen shayi da ababen hawa daga Brazil da Canada”.

Sanarwar ta ƙara da cewa a filin jirgin saman Enugu an kama wani fasinja mai suna Eze Christian Ikenna mai shekara 42, da ya shiga ƙasar daga Brazil ranar 20 ga watan Janairun, bayan da aka binciki jakar da ya zo da ita inda ka samu hodar ibilis da ta kai nauyin kiligiram 16.2.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp