Jamiāan hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, sun damke mutane a manyan filayen jiragen sama guda uku na kasar ciki akwai Legas, Abuja da kuma Fatakwal da manyan odar iblis da masu safarar miyagun kwayoyi na Brazil suka yi kokarin shiga da su Najeriya.
A cewar mai magana da yawun hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi, an kama wasu masu fataucin mutane 7 ne a cikin wannan farfagandar.
Sanarwar da kakakin ya fitar a ranar Lahadi ta ce, a filin jirgin sama na Fatakwal, an kama wasu mutane biyar da ake zargi a ranar Asabar 9 ga watan Afrilu.
An kama uku daga cikinsu a lokacin da ake tantance fasinjojin da ke cikin jirgin Qatar Airline QR1433 daga Doha zuwa Fatakwal.
Ya ce, wadanda ake zargin sun taso ne daga birnin Sao Paulo na kasar Brazil a cikin jirgin Qatar guda, da ke kan hanyar Doha zuwa Abuja da kuma Fatakwal dauke da kwayar hodar iblis mai nauyin kilogiram 24.96.