fidelitybank

NDLEA sun kama Matar da za ta yi safar hodar Iblis zuwa Iran

Date:

Jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya, NDLEA sun ce sun kama wata mata da ta yi yunkurin fita da hodar iblis zuwa ƙasar Iran.

Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Femi Babafemi ya fitar, ya ce an kama matar ce a filin jirgin sama a Fatakwal, babban birnin jihar Ribas – inda ta saka hodar iblis ɗin a cikin al’aurarta da cikinta da kuma a wata jaka.

Babafemi ya ce matar mai suna Ihensekhien Miracle Obehi, wadda ta saka hijabi domin ƙoƙarin tsallake binciken jami’an tsaro, an cafke ta ne a Lahadin da ya gabata lokacin da take yunkurin shiga jirgin Qatar Airline zuwa Doha, kafin ta wuce Iran.

Ya ƙara da cewa yayin bincike, an gano matar ta saka ƙunshin hodar iblis har uku cikin al’aurarta, sannan ta saka wani a jakarta sai kuma ta haɗiye ƙwayoyi 67 a cikinta.

Sakamakon haka, an tilasta ta yin aman ƙwayoyin da kuma wanda ta saka a cikinta da al’aurarta.

Obehi ta yi iƙirarin cewa an saka ta ta haɗiye ƙwayoyin hobar iblis 70, sai dai bayan haɗiye 67 ta ƙasa haɗiye sauran – inda ta yanke shawarar saka su a al’aurarta, a cewar Babafemi.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp