Babban jami’in ‘yan sandan Najeriya da aka dakatar ya musanta zargin alakanta shi da kungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ta ƙasa da ƙasa.
An kama Abba Kyari ne a makon da ya gabata bayan da hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta kasar NDLEA ta zarge shi da alaƙa da wata kungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi da ke aiki tsakanin Najeriya da Habasha da kuma Brazil.
Sai dai a ranar Litinin ya shaidawa wata kotu a Abuja babban birnin kasar ta hannun lauyoyinsa cewa ƙirƙirar zargin aka yi.
Hukumar NDLEA ta yi zargin cewa Mista Kyari ya yi yunkurin bai wa jami’anta cin hanci don kilo 25 na hodar ibilis da jami’ansa suka kama sannan suka raba.
Sai dai Abba Kyari ya musanta zargin cewa, jami’an hukumar NDLEA ne suka masa gadar zare bayan ya nace sai an bayar da lada ga wanda ya bayar da labarin da ya kai ga kama waɗanda ake zargi da safarar miyagun kwayoyi kamar yadda suka amince da farko.
Ɗaya daga cikin lauyoyinsa, Hamza Nuhu Dantani, ya shaida wa BBC cewa, sun kuma gabatar da bukatar neman belinsa.