Rahotanni sun bayyana cewa, mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da aka dakatar, Abba Kyari ya fadi wasu bayanai yayin da hukumar NDLEA ta yi masa tambayoyi.
Majiya a NDLEA ta ce, mganarsa za ta kai ga ci gaba da gudanar da bincike, lamarin da ya sa hukumar ta garzaya kotu, domin ba ta damar tsare Kyari da sauran mutanensa hudu.
Rundunar ‘yan sanda a ranar Litinin, 14 ga watan Fabrairu, ta kama Kyari da wasu mutane hudu tare da mika su ga NDLEA, bayan zarginsu da hannu a safarar miyagun kwayoyi.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa Abba Kyari, mataimakin kwamishinan ‘yan sanda da aka dakatar tare da wasu ‘yan tawagarsa mutane hudu na iya ci gaba da zama a hannun hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA).
Da take zantawa da wata majiya mai tushe a hukumar, Punch ta bayyana cewa, Kyari ya yi wasu bayanai da za su kai ga kara bincike, domin haka hukumar ta NDLEA ba za ta iya gurfanar da shi a gaban kuliya ba.
An kuma bayyana cewa, tuni hukumar ta NDLEA ta fara gudanar da bincike kan hodar iblis da babban jami’in ‘yan sandan ya nemi kulla harkallarta.