fidelitybank

NCC ta rufe layukan wayoyi sama da miliyan 11 a Najeriya

Date:

Hukumar da ke sa ido kan harkar sadarwa ta kasa NCC, ta tabbatar da rufe layukan masu wayoyin salular da basu haɗa da lambar shaidar zama ɗanƙasa ba.

A makon da ya wuce ne hukumar ta bai wa kamfanonin wayoyin salula umarnin rufe layin duk wani wanda bai haɗa layin wayarsa da NIN ba ya zuwa ranar 28 ga watan Fabairun, 2024.

Wasu kafofin watsa labarai na ƙasar sun ce waɗanda lamarin ya shafa sun kai miliyan 11 da dubu 200.

Sai dai wata hira da wani gidan talabijin na cikin ƙasar, kakakin hukumar , Reuben Muoka ya ce zai yi wuya a ce ga yawan layukan da aka rufe, amma NCC za ta yi kididdiga kafin ƙarshen wannan makon, bayan sun samu alƙaluma daga kamfanonin sadarwar.

“A ɗauka cewa duk wani wanda bai bayar da NIN ɗinsa ba an rufe layinsa. A haƙiƙanin gaskiya ma tun kafin cikar wa’adin wasu kamfanonin sadarwan suka fara rufe layukan mutane. Ya shaida wa Channels TV.

Haka kuma ya yi tsokaci kan wasu masu wayoyin da suka ce sun riga sun haɗa NIN ɗinsu da lauyukansu amma duk da hakan an rufe layukansu, inda ya ce an rufe wasu layukan ne saboda ta yiwu NIN ɗin da suka bayar bai zo daidai da wanda suka yi rajista ba.

Masu irin waɗan nan matsaloli a cewarsa, dole su je kamfanonin sadarwar da kansu domin a gyara matsalolin.

A baya dai hukumar ta sha sanya ranar rufe layukan mutanen da basu haɗa da lambar shaidar zama ɗanƙasar ba, sai dai a wannan karon ta ce babu batun ɗagewa.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp