Hukumar Sadarwa ta kasa (NCC) ta ce, kasar za ta karbi kebir na karkashin ruwa na Google manhajar (Equiano) kafin karshen watan Afrilu.
Ikechukwu Adinde, daraktan hulda da jama’a na NCC ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, bayan da Google Global Services Nigeria ya kai ziyarar ban girma ga hukumar.
A cewar sanarwar, NCC ta ce Google ya bayyana kudirinsa na yin aiki tare da hukumar wajen ciyar da ayyukan samar da hanyoyin sadarwa na duniya gaba da inganta manufofin sauyin zamani na kasar.
Da yake karbar tawagar Google, Umar Danbatta, mataimakin shugaban zartarwa na NCC, ya ce, hukumar na fatan ganin shirye-shiryen bangarorin biyu sun yi tasiri ta hanyar inganta hadin gwiwa tsakanin NCC da Google Nigeria don yin tasiri mai adadi da yawa.