fidelitybank

NCAA ta rufe babbar cibiyar Globacom saboda taurin bashi

Date:

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya NCAA ta ce, ta rufe ainihin babbar cibiyar kamfanin Globacom Limited da ke Wuse 2, Abuja, saboda rashin biyan bashin Naira biliyan 4.7, bisa gaggarumin matsin lamba da gwamnatin tarayya ta yi.

Babban daraktan hukumar ta NCAA, Musa Nuhu, ya gudanar da atisayen ne a ranar Laraba a karkashin kulawar ministan sufurin jiragen sama Hadi Sirika.

Ya kuma ce,”Hukumar tawa ta na fuskantar matsananciyar matsin lamba daga gwamnatin tarayyar Najeriya, kuma za mu yi iya kokarinmu a kan ikon da a ka ba mu, domin ganin an warware biyan basussukan,” inji Nuhu .

Ya kuma shaida wa manema labarai bayan ya kulle ginin cewa, za a sauya wurin ne har sai Globacom ya biya bashin.

Ya bayyana cewa, kamfanin ya biya Naira miliyan 500 ne kawai daga cikin Naira biliyan 5.2 da ya ke bi, inda ya nuna cewa bashin da a ke bin ya kai Naira biliyan 4.7.

A cewarsa, sauran kamfanonin sadarwa su na biya sai dai kamfanin Globacom, wanda ya kasa hadawa tun 2007.

sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp