Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya NCAA ta ce, ta rufe ainihin babbar cibiyar kamfanin Globacom Limited da ke Wuse 2, Abuja, saboda rashin biyan bashin Naira biliyan 4.7, bisa gaggarumin matsin lamba da gwamnatin tarayya ta yi.
Babban daraktan hukumar ta NCAA, Musa Nuhu, ya gudanar da atisayen ne a ranar Laraba a karkashin kulawar ministan sufurin jiragen sama Hadi Sirika.
Ya kuma ce,”Hukumar tawa ta na fuskantar matsananciyar matsin lamba daga gwamnatin tarayyar Najeriya, kuma za mu yi iya kokarinmu a kan ikon da a ka ba mu, domin ganin an warware biyan basussukan,” inji Nuhu .
Ya kuma shaida wa manema labarai bayan ya kulle ginin cewa, za a sauya wurin ne har sai Globacom ya biya bashin.
Ya bayyana cewa, kamfanin ya biya Naira miliyan 500 ne kawai daga cikin Naira biliyan 5.2 da ya ke bi, inda ya nuna cewa bashin da a ke bin ya kai Naira biliyan 4.7.
A cewarsa, sauran kamfanonin sadarwa su na biya sai dai kamfanin Globacom, wanda ya kasa hadawa tun 2007.