Hukumar da ke kula da kafofin yada labarai ta NBC, ta ci tarar gidan talabijin na Arise naira miliyan biyu bayan samunta da laifin yaɗa kalaman da za su tunzura ‘yan ƙasa.
A cikin wata sanarwa da NBC ta fitar wadda ta samu sa hannun shugaban hukumar Balarabe Shehu Ilelah, ta ce an kama gidan talabijin ɗin da laifi ne bayan da ya watsa wata magana da gwamnan jihar Rivers Nyesom Wike ya yi a ranar 24 a watan Febrairu, inda yake suka ga magoya bayan jam’iyyar APC.
NBC ta ce a cikin maganganu da Wike ya yi ya ce “Ni ba ɗan APC bane kuma ba zan shiga jam’iyyar ba, amma sun sanya na amince da su a matsayin jajirtattu, don haka mulki ya koma kudu”.
Sanarwar ta NBC ta ƙara da cewa Arise ya kuma saka wata tattaunawa da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC a daidai lokacin da ake kaɗa kuri’a a ranar zaɓe wanda abu ne da ya saɓawa dokokin hukumar.
Har ila yau, ta ce gidan talabijin ɗin ya gayyato baki da dama waɗanda suka yi kalamai na tunzura ‘yan ƙasa zuwa cikin rikici.
NBC ta kuma ce cikin laifukan da Arise ya yi, akwai saka wakar wani ɗan Najeriya mai suna Fela Kuti da ke magana kan batun maguɗin zaɓe da kuma cin hanci, inda ta ce bai kamata gidan talabijin ɗin ya saka wakar a lokacin ba saboda ana cikin zaɓe.
A don haka, NBC ta ce ta ci tarar gidan talabijin naira miliyan biyu saboda aikata waɗannan laifuka da suka saɓawa dokokin kafafen yaɗa labaru a ƙasar.