fidelitybank

NBC ta ci tarar Talabinjin din Arise a kan kalaman tunziri

Date:

Hukumar da ke kula da kafofin yada labarai ta NBC, ta ci tarar gidan talabijin na Arise naira miliyan biyu bayan samunta da laifin yaɗa kalaman da za su tunzura ‘yan ƙasa.

A cikin wata sanarwa da NBC ta fitar wadda ta samu sa hannun shugaban hukumar Balarabe Shehu Ilelah, ta ce an kama gidan talabijin ɗin da laifi ne bayan da ya watsa wata magana da gwamnan jihar Rivers Nyesom Wike ya yi a ranar 24 a watan Febrairu, inda yake suka ga magoya bayan jam’iyyar APC.

NBC ta ce a cikin maganganu da Wike ya yi ya ce “Ni ba ɗan APC bane kuma ba zan shiga jam’iyyar ba, amma sun sanya na amince da su a matsayin jajirtattu, don haka mulki ya koma kudu”.

Sanarwar ta NBC ta ƙara da cewa Arise ya kuma saka wata tattaunawa da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC a daidai lokacin da ake kaɗa kuri’a a ranar zaɓe wanda abu ne da ya saɓawa dokokin hukumar.

Har ila yau, ta ce gidan talabijin ɗin ya gayyato baki da dama waɗanda suka yi kalamai na tunzura ‘yan ƙasa zuwa cikin rikici.

NBC ta kuma ce cikin laifukan da Arise ya yi, akwai saka wakar wani ɗan Najeriya mai suna Fela Kuti da ke magana kan batun maguɗin zaɓe da kuma cin hanci, inda ta ce bai kamata gidan talabijin ɗin ya saka wakar a lokacin ba saboda ana cikin zaɓe.

A don haka, NBC ta ce ta ci tarar gidan talabijin naira miliyan biyu saboda aikata waɗannan laifuka da suka saɓawa dokokin kafafen yaɗa labaru a ƙasar.

nigeria news today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp