fidelitybank

Natasha ta halarci zaman kotu tsakanin ta da Akpabio

Date:

Sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya a majalisar dattijai, Natasha Akpoti-Uduaghan ta halarci zaman kotu a shari’ar da take ƙalubalantar dakatarwar da aka yi mata daga majalisar.

A watan Maris ne majalisar dattijan ta dakatar da Natasha bisa zargin rashin ɗa’a bayan taƙaddamar da ta kaure tsakaninta da shugaban majalisar Godswill Akpabio.

A cikin ƙorafinta, Natasha ta haɗa majalisar tarayya da majalisar dattawa da shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio, da kuma Sanata Neda Imasuen, shugaban kwamitin majalisar dattawa kan ladabi da haƙƙoƙi da ɗabi’a a matsayin waɗanda ake ƙara.

Lokacin da aka kira shari’ar, wadda aka mayar a hannun Justice Binta Nyako bayan Justice Obiora Egwuatu ya janye daga sauraron ta, lauyan Sanata Natasha, Jibrin Okutekpa, ya shaida wa kotu cewa sun gabatar da dukkan takardun da za su dogara da su a shari’ar, kamar yadda kotu ta umarta a zaman da ya gabata.

Lauyoyin da ke wakiltar majalisar dattawa, Paul Daudu, da na shugaban majalisar, Ekwo Ejembi, su ma sun shaida wa kotu cewa sun gabatar da takardun da za su dogara da su. Amma sun jawo hankalin kotun kan wani buƙata da suka shigar dangane da rashin bin umarnin kotu da suke zargin wanda ke karar da aikatawa.

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, a cikin wa’adin martaninta na ƙari, ta zargi shugaban majalisar dattawa da ƙoƙarin tauye mata haƙƙinta na faɗin albarkacin baki

Ta ce wasikar da ta rubuta kwanan nan zuwa ga shugaban majalisar dattawa ba ta karya umarnin kotu ba, wanda ya haramta wa ɓangarorin da ke cikin shari’ar yin magana da kafafen yaɗa labarai.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp