Sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya a majalisar dattijai, Natasha Akpoti-Uduaghan ta halarci zaman kotu a shari’ar da take ƙalubalantar dakatarwar da aka yi mata daga majalisar.
A watan Maris ne majalisar dattijan ta dakatar da Natasha bisa zargin rashin ɗa’a bayan taƙaddamar da ta kaure tsakaninta da shugaban majalisar Godswill Akpabio.
A cikin ƙorafinta, Natasha ta haɗa majalisar tarayya da majalisar dattawa da shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio, da kuma Sanata Neda Imasuen, shugaban kwamitin majalisar dattawa kan ladabi da haƙƙoƙi da ɗabi’a a matsayin waɗanda ake ƙara.
Lokacin da aka kira shari’ar, wadda aka mayar a hannun Justice Binta Nyako bayan Justice Obiora Egwuatu ya janye daga sauraron ta, lauyan Sanata Natasha, Jibrin Okutekpa, ya shaida wa kotu cewa sun gabatar da dukkan takardun da za su dogara da su a shari’ar, kamar yadda kotu ta umarta a zaman da ya gabata.
Lauyoyin da ke wakiltar majalisar dattawa, Paul Daudu, da na shugaban majalisar, Ekwo Ejembi, su ma sun shaida wa kotu cewa sun gabatar da takardun da za su dogara da su. Amma sun jawo hankalin kotun kan wani buƙata da suka shigar dangane da rashin bin umarnin kotu da suke zargin wanda ke karar da aikatawa.
Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, a cikin wa’adin martaninta na ƙari, ta zargi shugaban majalisar dattawa da ƙoƙarin tauye mata haƙƙinta na faɗin albarkacin baki
Ta ce wasikar da ta rubuta kwanan nan zuwa ga shugaban majalisar dattawa ba ta karya umarnin kotu ba, wanda ya haramta wa ɓangarorin da ke cikin shari’ar yin magana da kafafen yaɗa labarai.