fidelitybank

Natasha ta halarci zaman kotu tsakanin ta da Akpabio

Date:

Sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya a majalisar dattijai, Natasha Akpoti-Uduaghan ta halarci zaman kotu a shari’ar da take ƙalubalantar dakatarwar da aka yi mata daga majalisar.

A watan Maris ne majalisar dattijan ta dakatar da Natasha bisa zargin rashin ɗa’a bayan taƙaddamar da ta kaure tsakaninta da shugaban majalisar Godswill Akpabio.

A cikin ƙorafinta, Natasha ta haɗa majalisar tarayya da majalisar dattawa da shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio, da kuma Sanata Neda Imasuen, shugaban kwamitin majalisar dattawa kan ladabi da haƙƙoƙi da ɗabi’a a matsayin waɗanda ake ƙara.

Lokacin da aka kira shari’ar, wadda aka mayar a hannun Justice Binta Nyako bayan Justice Obiora Egwuatu ya janye daga sauraron ta, lauyan Sanata Natasha, Jibrin Okutekpa, ya shaida wa kotu cewa sun gabatar da dukkan takardun da za su dogara da su a shari’ar, kamar yadda kotu ta umarta a zaman da ya gabata.

Lauyoyin da ke wakiltar majalisar dattawa, Paul Daudu, da na shugaban majalisar, Ekwo Ejembi, su ma sun shaida wa kotu cewa sun gabatar da takardun da za su dogara da su. Amma sun jawo hankalin kotun kan wani buƙata da suka shigar dangane da rashin bin umarnin kotu da suke zargin wanda ke karar da aikatawa.

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, a cikin wa’adin martaninta na ƙari, ta zargi shugaban majalisar dattawa da ƙoƙarin tauye mata haƙƙinta na faɗin albarkacin baki

Ta ce wasikar da ta rubuta kwanan nan zuwa ga shugaban majalisar dattawa ba ta karya umarnin kotu ba, wanda ya haramta wa ɓangarorin da ke cikin shari’ar yin magana da kafafen yaɗa labarai.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp