fidelitybank

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Date:

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar da komawa bakin aiki, inda ta bayyana cewa ba ta da hurumin komawa har sai an kawo ƙarshen dakatarwar da aka yi mata.

A wata sanarwa da kakakin majalisar, Yemi Adaramodu ya fitar ranar Lahadi, ya jaddada cewa babu wani umarnin kotu da ya ce majalisar ta karɓi Sanata Natasha kafin ƙarewar lokacin da aka dakatar da ita.

An dakatar da sanata Natasha ne tun watan Maris ɗin 2025 sakamakon karya dokokin majalisar bayan ta yi gardama da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio – inda ta zarge shi da cin zarafi ta hanyar lalata, abin da Akpabio ya musanta.

A kwanakin baya, Natasha, wadda ta dogara da hukuncin da mai shari’a Binta Nyako na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke, ta bayyana niyyarta ta komawa zauren majalisa ranar Talata, 22 ga Yuli, 2025.

Sai dai, kakakin majalisar dattawa ya ce hukuncin ba ya ɗauke da wani umarni na doka da ya ce majalisar ta karɓi dawowar sanatar kafin karewar wa’adin dakatarwa da aka yi mata.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp