Ɗan takarar shugaban ƙasa a Najeriya na jam’iyyar Labour a zaɓukan 2023, Peter Obi, ya ce hukuncin Kotun Koli ba shi ne karshen siyasarsa ba.
Obi ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai da ya kira a yau Litinin a Abuja, inda ya ce shi da magoya bayansa waɗanda ake kira “Obedient Movement” sun zama ƴan adawa a siyasar Najeriya.
“Muradina shi ne samar da sabuwar Najeriya kuma hakan ba zai sauya ba duk da hukuncin da Kotun Koli ta yanke a ranar 26 ga watan Oktoba,” in ji shi.
Ya ce “yadda abubuwa ke tafiya a ƙasar nan, su suka saka muka fito domin zama ƴan adawa a ɓangaren siyasar ƙasar, saboda tana son samun ƴan adawa masu karfi.
Obi ya ce Kotun ta yi watsi da shaida ta yankan shakku, kamar kin amfani da dokokin zaɓe da ya ce INEC ba ta yi ba, abu kuma da ya ce bai kamata hukumar zaɓen tayi wasa da shi ba.