fidelitybank

Nasarar NNPP a Kano tarihi ne ya maimaita kansa – Kwankwaso

Date:

Jagoran jam’iyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ce zaɓen ƙananan hukumomin da jam’iyarsa ta gudanar a Kano tarihi ne ya maimaita kansa, “Ba a daki kowa ba, ba a zagi kowa ba, babu wani faɗace-faɗace.”

Kwankwaso ya ce sun san cewa jam’iyun hammaya na iya daukar matakin shari’a shiyasa suma ba su bari an bar su a baya ba.

“Hukumomin Kano sun san halin wadansu musamman ƴan APC, shiyasa hukumar garzaya kotu saboda ta samu kariya, daman an sanya rai za ayi irin wannan, aka bada hukunci mai ƙwarin gaske wanda ya sanya wa duk wanda zai kawowa dimokradiyya cikasa takunkumi,” Cewar Kwankwaso.

Sanata Rabi’u Musa ya ce duk wadanda suke ƙoƙarin rikita jam’iyyar hadin baki ne domin a haifar masu da rudani da rikici cikin jam’iyarsu.

A yau Litinin ne ake sa ran shugabannin ƙananan hukumomin jihar Kano 44, za su shiga ofis domin fara aiki gadan-gadan, bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf ya rantsar da su a ranar Lahadi.

An gudanar da bikin rantsarwar a fadar gwamnatin jihar, a gaban manyan ƙusoshin gwamnatin jihar da wakilin sarkin Kano da sarakunan Gaya da Rano da Karaye

Zaɓen jihar Kano na ƙarshen makon jiya, ya zo da matuƙar taƙaddama, inda babbar jam’iyyar adawa a jihar, wato APC ta samo umarnin kotu da ya rusa shugabancin hukumar zaɓen Kano.

Hukumar zaɓen jihar ta bayyana jam’iyyar NNPP mai mulkin jihar da lashe zaɓen duka shugabannin ƙananan hukumomin jihar 44 da kansiloli 484.

Jami’iyyar APC mai hamayya a jihar ba ta shiga zaɓen ba.

A ranar Talatar ne wata babbar Kotun tarayya a kano ƙarƙashin jagorancin mai shari’a Simon Amobeda ta rushe shugabancin hukumar zaɓe ta jahar Kano bisa dogaro da hujjojin da aka gabatar mata na rashin cancantar shugabannin hukumar bisa kasancewarsu ƴan siyasa masu ɗauke da katin Jam’iyyar NNPP.

Wani ɗan jam’iyyar APC Hon Aminu Tiga da Jam iyyarsa ta APC ne dai suka shigar da ƙara inda suka roƙi kotun da ta rushe shugabannin hukumar zaɓen ta Kano bisa kasancewrsu ƴan jam’iyya mai mulki.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp