fidelitybank

Nasarar NNPP a Kano tarihi ne ya maimaita kansa – Kwankwaso

Date:

Jagoran jam’iyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ce zaɓen ƙananan hukumomin da jam’iyarsa ta gudanar a Kano tarihi ne ya maimaita kansa, “Ba a daki kowa ba, ba a zagi kowa ba, babu wani faɗace-faɗace.”

Kwankwaso ya ce sun san cewa jam’iyun hammaya na iya daukar matakin shari’a shiyasa suma ba su bari an bar su a baya ba.

“Hukumomin Kano sun san halin wadansu musamman ƴan APC, shiyasa hukumar garzaya kotu saboda ta samu kariya, daman an sanya rai za ayi irin wannan, aka bada hukunci mai ƙwarin gaske wanda ya sanya wa duk wanda zai kawowa dimokradiyya cikasa takunkumi,” Cewar Kwankwaso.

Sanata Rabi’u Musa ya ce duk wadanda suke ƙoƙarin rikita jam’iyyar hadin baki ne domin a haifar masu da rudani da rikici cikin jam’iyarsu.

A yau Litinin ne ake sa ran shugabannin ƙananan hukumomin jihar Kano 44, za su shiga ofis domin fara aiki gadan-gadan, bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf ya rantsar da su a ranar Lahadi.

An gudanar da bikin rantsarwar a fadar gwamnatin jihar, a gaban manyan ƙusoshin gwamnatin jihar da wakilin sarkin Kano da sarakunan Gaya da Rano da Karaye

Zaɓen jihar Kano na ƙarshen makon jiya, ya zo da matuƙar taƙaddama, inda babbar jam’iyyar adawa a jihar, wato APC ta samo umarnin kotu da ya rusa shugabancin hukumar zaɓen Kano.

Hukumar zaɓen jihar ta bayyana jam’iyyar NNPP mai mulkin jihar da lashe zaɓen duka shugabannin ƙananan hukumomin jihar 44 da kansiloli 484.

Jami’iyyar APC mai hamayya a jihar ba ta shiga zaɓen ba.

A ranar Talatar ne wata babbar Kotun tarayya a kano ƙarƙashin jagorancin mai shari’a Simon Amobeda ta rushe shugabancin hukumar zaɓe ta jahar Kano bisa dogaro da hujjojin da aka gabatar mata na rashin cancantar shugabannin hukumar bisa kasancewarsu ƴan siyasa masu ɗauke da katin Jam’iyyar NNPP.

Wani ɗan jam’iyyar APC Hon Aminu Tiga da Jam iyyarsa ta APC ne dai suka shigar da ƙara inda suka roƙi kotun da ta rushe shugabannin hukumar zaɓen ta Kano bisa kasancewrsu ƴan jam’iyya mai mulki.

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp