Hukumar da ke yaƙi da fataucin mutane ta Najeriya, NAPTIP ta ce ta kuɓutar da wasu ƴan Najeriya da aka yi niyyar safararsu zuwa Libya.
Kwamandan hukumar a jihar Zamfara, Aliyu Abubakar ya bayyana cewa an samu nasarar ceto mutanen tara ne a iyakar Babura da ke jihar Jigawa, kamar yadda gidan talabijin na Channels a Najeriya ya ruwaito.
Aliyu ya ce akwai mata guda uku cikin mutanen tara – waɗanda ƴan asalin jihar Zamfara ne.
Sun tserewa gidajensu ne sakamakon hare-haren ƴanbindiga, inda suka koma zama a Kaduna.
NAPTIP ta ja hankalin mutane kan faɗawa makomar masu safarar mutane – inda ta ce kowa ya yi taka tsantsan.
Safarar mutane dai ba sabon abu bane a kan iyakokin Najeriya, inda a watan Fabrairu, gwamnatin jihar Neja ta karɓi yara 21 da hukumar shige da fice ta kuɓutar da su – waɗanda ba su haura shekara tara ba lokacin da ake tafiya da su Nijar.