Hukumar hana fataucin mutane ta kasa (NAPTIP), reshen jihar Kano, ta sake hada Isma’il Sabo mai shekaru 12 da mahaifiyarsa, shekara daya bayan an bayyana bacewarsa.
Kwamandan hukumar na shiyyar, Abdullahi Babale, ya mika Isma’il ga mahaifiyarsa ranar Alhamis.
Ya bayyana cewa, an ceto wanda abin ya rutsa da shi, kuma jami’an tsaro na jihar Kano sun mikawa hukumar, domin sake haduwa da iyalansa.
A cewar Babale, Isma’il ya shafe wata guda tare da hukumar a matsugunin su.
Maryam Muhammed, ta yaba da kokarin hukumomi daban-daban da suka ceto danta.
Ta yarda cewa iyaye suna da rawar da zasu taka wajen tabbatar da tsaron ’ya’yansu daga mutanen da suka saba yaudararsu.