fidelitybank

NAPTIP ta ceto ƴar shekara biyu da aka sayar kan 100,000 a Abuja

Date:

Hukumar da ke yaƙi da fataucin mutane a Najeriya, NAPTIP ta ce ta ceto wata yarinya ƴar shekara biyu da aka yi safararta zuwa jihar Abia daga Abuja.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar ranar Juma’a, ta ce hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ne suka kama wanda ya yi safararta, inda ake zargin ya sayar da da ita kan naira 100,000.

“Mun samu nasarar ceto Chiamaka Favor, bayan safararta daga Abuja zuwa Aba a watan Febrairun 2025.

“Ana zargin wanda ya yi safararta ya yi aiki da wasu ƙungiyoyin safarar mutane uku a Abuja – sannan ya sayar da ita ga wani kan naira 100,000. Muna ci gaba da bincike,” in ji NAPTIP.

Hukumar ta kuma yi kira ga iyayen yarinyar ko ƴan uwanta da su hanzarta su tuntuɓe ta domin karɓar ƴarsu.

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp