fidelitybank

Nan gaba kadan za ku ji dalilan da ya sa APC muka rasa Kano – APC

Date:

Bayan yanke hukuncin ƙarshe da Kotun ƙolin Najeriya ta yi, wanda ya tabbatar da kujerun gwamnonin jahohin adawa na Kano da Zamfara da Filato da Bauchi, jam’iyyar APC mai mulki a ƙasar ta ce hakan bai razana ta ba.

Jami’yyar ta ce akwai rata mai nisa tsakaninta da sauran jam’iyyun adawa kasancewar yawan jihohin da take da su, duk da ana ganin nasarorin da jam’yyun adawar suka samu a kotun koli ta kara masu karfi.

A wata hirar da ya yi da BBC wani jigon jam’iyyar ta APC kuma , karamin ministan gidaje da raya birane Injiniya Abdullahi Tijjani Gwarzo ya ce duk wani gunagunin da ake yi lokaci ne zai tabbatar da asalin yadda lamura suke da kuma irin ƙarfin da jam’iyyar take da shi a siyasance.

Ministan ya ce duk maganganun da ake ta yaɗawa game da jam’iyyar gabannin yanke hukuncin kotun duk labarai ne na ƙanzon-kurege, kuma asalin bayanai za su bayyana nan gaba.

‘Ana cewa mun rasa Jihohi, ai ba rasa su muka yi ba, harka ce ta kotu, abin da kotu ta zo da shi, mu ma mun shiga kuma an shigar da mu, saboda haka mun yi nasara a wasu kuma a wasu mun yi rashin nasara. Yanzu APC muna da jiha 20 mai bi mana PDP tana da 13, APGA na da ɗaya Labour na da ɗaya, NNPP na da ɗaya, to me za mu ƙyasa a ciki? Jn ji shi.

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp