fidelitybank

Nan gaba kaɗan za mu ƙwace Rivers duk da rikicin Wike da Fubara – APC

Date:

Jam’iyyar APC mai mulki ta bayyana kwarin gwiwar cewa, nan ba da dadewa ba za ta karbe iko da jihar Ribas.

Shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Ganduje ne ya bayyana haka a wani taron da aka gudanar ranar Alhamis a Abuja.

Ganduje ya jaddada cewa za a sake gina reshen jam’iyyar a jihar Ribas tare da mayar da hankali wajen kafa sansani a jihar.

Ganduje ya bayyana haka ne a lokacin da dan takarar gwamna na jam’iyyar Action Alliance (AA) a 2023, Dawari Ibietela George, ya koma APC a hukumance.

A yayin tattaunawar tasu, shugabannin sun mayar da hankali ne wajen sake gina jam’iyyar reshen Jihar Ribas tare da mayar da ita wani dandali na yi wa al’ummar jihar da kasa hidima yadda ya kamata.

Ganduje ya bayyana kudirin jam’iyyar na rungumar bukatu daban-daban tare da tabbatar da adalci.

Ya bayyana George a matsayin babban kifi, ya kuma yaba wa hazakarsa ta siyasa, inda ya nuna kwarin gwiwa kan yadda zai kara karfin jam’iyyar.

Ganduje ya yi maraba da George, inda ya tabbatar masa da cewa za a kafa wani tsari mai inganci da zai dauki nauyinsa da sauran mambobin da suka dawo.

“Jihar Rivers za ta zama jam’iyyar APC gaba daya. Yanzu kun kasance daidai da kowane dan jam’iyya. Mun himmatu wajen fadada dimokuradiyya a kasar nan,” Ganduje ya kara da cewa.

Kalaman nasa na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da gwabza fada tsakanin gwamnan jihar, Sim Fubara da kuma magabacinsa, Nyesom Wike, wanda a yanzu yake rike da mukamin ministan babban birnin tarayya karkashin gwamnatin APC, dangane da wanene ke rike da tsarin jam’iyyar a jihar.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp