fidelitybank

Nan da sa’o’i 48 za mu fara sayar da fetur amma farashin na wuyan NNPCL – Dangote

Date:

Shugaban Rukunin Dangote, Aliko Dangote, ya bayyana cewa, za a samar da Man Fetur (Premium Motor Spirit) a kasuwannin Najeriya nan da sa’o’i 48, ya danganta da Kamfanin Man Fetur na Najeriya.

Attajirin da ya fi kowa kudi a Afirka ya bayyana hakan ne a ranar Talata a wata hira da gidan talabijin na Channels, yayin da a hukumance ya sanar da fara fara fitar da man fetur daga matatar mai da ke Legas 650,000 a kowace rana ranar Talata a Legas.

Ya jaddada cewa nan ba da jimawa ba matatar mai na dala biliyan 20 za ta kammala tattaunawa da kamfanin na NNPC domin isar da kayan ga ‘yan Najeriya.

Da yake magana kan farashin man fetur din Dangote ya bayyana cewa shi ne tsarin majalisar zartarwa ta tarayya karkashin jagorancin shugaba Bola Ahmed Tinubu ne za ta yanke hukunci.

“PMS na iya kasancewa a gidajen mai a cikin sa’o’i 48 masu zuwa, ya danganta da NNPCPL.

“A kan farashin PMS, tsari ne wanda Majalisar Zartarwa ta Tarayya karkashin jagorancin Mai Girma, Bola Ahmed Tinubu ta tsara kuma ta amince da shi. Da zaran an kammala, wanda shi ne abin da yake turawa da zarar ya kammala taron FEC, zai iya zama yau ko gobe a shirye mu ke mu fito kasuwa.” Inji shi.

Tun da farko dai Dangote a hukumance ya sanar da fara fitar da mai a ranar Talata.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp