fidelitybank

Nan ba da jimawa ‘yan Najeriya za su ci gajiyar rarar talafin fetur – Gwamnan Gombe

Date:

Gwamna Inuwa Yahaya na jihar Gombe, a ranar Talata, ya ce nan ba da dadewa ba ‘yan Najeriya za su ci gajiyar rarar tallafin man fetur.

Yahaya ya bayyana hakan ne a Gombe yayin da yake kaddamar da kashi na biyu na rabon tallafin jin kai ga mazauna jihar.

Ya bayyana cewa shugaban kasa Bola Tinubu tare da hadin gwiwar gwamnonin jihohi na kara zage damtse wajen ganin an kawo karshen wahalhalun da ake samu sakamakon cire tallafin man fetur.

Ya ce ana zuba jari da dama da nufin fitar da ‘yan Najeriya daga halin kuncin da suke ciki na tattalin arziki.

“Addu’ar mu ce wannan abu (wahala) ya kare da yardar Allah kuma da kudurin Shugaban kasa da gwamnoni, za mu tabbatar da cewa Nijeriya ta samu kwanciyar hankali.

“Za mu yi sauri da sauri don kawo karshen wahalhalun da cire tallafin ya haifar.

“Babban dalilin da ya jawo wahalhalu shi ne janye tallafin man fetur amma daga yau matatar mai ta Fatakwal tana ci gaba da hakowa.

“Nan ba da jimawa ba za mu samu albarkatun man fetur din da aka tace a cikin gida ya kai ga jama’a kuma babu dalilin da zai sa irin wadannan kayayyakin da ake kerawa a cikin gida za su yi tsada kamar abin da ya kashe mutane a yanzu,” inji shi.

Gwamnan ya yabawa mazauna jihar da ‘yan Najeriya bisa hakurin da suka yi tun bayan cire tallafin tare da ba su tabbacin kwana mai kyau a gaba.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp