fidelitybank

Nan ba da jimawa ba za mu kawo karshen matsalar tsaro – Sojoji

Date:

Babba hafsan sojojin ƙasa, Laftanar Janar, Taoreed Lagbaja ya tabbatar wa ‘yan ƙasar cewa nan ba da jimawa ba sojoji za su kawo karshen matsalar tsaron da ƙasar ke fuskanta.

Janar Lagbaja ya bayaya hakan ne cikin jawabin da ya yi a lokacin bikin rufe babban taron rundunar sojin ƙasa ta Najeriya na shekarar 2024 da aka gudanar a jihar Akwa ibom da ke kudancin ƙasar.

Taron na kwanaki biyar – wanda manyan hafsosjin rundunar sojin ƙasa ta Najeriya suka halarta ya duba irin nasarori da rundunar ke samu, da kuma irin tsare-tsare da rundunar ke yi wajen gudanar da ayyukanta a faɗin ƙasar..

”Ina son tabbatar muku cewa rundunar sojin ƙasa ta Najeriya na kan hanyar kawo ƙarshen matsalar tsaro da Najeriya ke fuskanta”, in ji Janar Lagbaja.

Ya ƙara da cewa ya samu wannan tabbaci ne sakamakon irin bayanan da yake samu daga sassa daban-daban na rundunar a faɗin ƙasar.

Tun da farko babban hafsan sojin ƙasan ya yi watsi da kiraye-kirayen da ya ce wasu da ya kira ”masu son rai na yi wa sojoji na kawo ƙarshen mulkin dimokraɗiyya”.

Ya ce a yanzu abin da ke gaban rundunar sojin Najeriya shi ne maido ta martaba ta ƙimarta, bayan shafe shekaru masu yawa suna jagorantar ƙasar, don haka ya ce sojojin ƙasar ba za su yi abin da zai zubar musu da ƙimar da suka yi shekara 25 suna ginawa kansu ta hanyar barin wanzuwar mulkin dimokraɗiyya a ƙasar.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp