fidelitybank

Nan ba da jimawa ba za mu kawo karshen matsalar tsaro – Sojoji

Date:

Babba hafsan sojojin ƙasa, Laftanar Janar, Taoreed Lagbaja ya tabbatar wa ‘yan ƙasar cewa nan ba da jimawa ba sojoji za su kawo karshen matsalar tsaron da ƙasar ke fuskanta.

Janar Lagbaja ya bayaya hakan ne cikin jawabin da ya yi a lokacin bikin rufe babban taron rundunar sojin ƙasa ta Najeriya na shekarar 2024 da aka gudanar a jihar Akwa ibom da ke kudancin ƙasar.

Taron na kwanaki biyar – wanda manyan hafsosjin rundunar sojin ƙasa ta Najeriya suka halarta ya duba irin nasarori da rundunar ke samu, da kuma irin tsare-tsare da rundunar ke yi wajen gudanar da ayyukanta a faɗin ƙasar..

”Ina son tabbatar muku cewa rundunar sojin ƙasa ta Najeriya na kan hanyar kawo ƙarshen matsalar tsaro da Najeriya ke fuskanta”, in ji Janar Lagbaja.

Ya ƙara da cewa ya samu wannan tabbaci ne sakamakon irin bayanan da yake samu daga sassa daban-daban na rundunar a faɗin ƙasar.

Tun da farko babban hafsan sojin ƙasan ya yi watsi da kiraye-kirayen da ya ce wasu da ya kira ”masu son rai na yi wa sojoji na kawo ƙarshen mulkin dimokraɗiyya”.

Ya ce a yanzu abin da ke gaban rundunar sojin Najeriya shi ne maido ta martaba ta ƙimarta, bayan shafe shekaru masu yawa suna jagorantar ƙasar, don haka ya ce sojojin ƙasar ba za su yi abin da zai zubar musu da ƙimar da suka yi shekara 25 suna ginawa kansu ta hanyar barin wanzuwar mulkin dimokraɗiyya a ƙasar.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp