fidelitybank

Nan ba da jimawa ba za a sake ni – Shugaban Awaren Biafara

Date:

Shugaban kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra, IPOB, Mazi Nnamdi Kanu, ya ce yana da yakinin za a bayar da belinsa a cikin watan Afrilu bayan ya shafe shekaru hudu yana tsare.

Kanu ya bayyana haka ne ga shugaban kungiyar al’ummar Igbo, ICA a Abuja, babban birnin tarayya, Engr. Ikenna Ellis-Ezenekwe, a lokacin da ya ziyarce shi a ofishin Hukumar DSS da ke Abuja, inda ake tsare da shi.

A cikin wata sanarwa da Ezenekwe ya fitar bayan ziyarar da ya kai wa shugaban kungiyar ta IPOB, ya tabbatar da cewa Kanu ya nuna rashin jin dadinsa kan rashin samun kwakkwaran jagoranci na kabilar Ibo tare da yin kira da a sake shi, yayin da ya kuma bukaci a sake yin kira ga yankin.

Ezenekwe, a cikin sanarwar manema labarai da ya raba wa DAILY POST, ya ce ya yi mamakin yadda Kanu ya kasance mai hazaka, abin dariya, har ma ya kara kiba duk da ciwon da ya sha.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “A yau a hedikwatar DSS da ke Abuja, na samu karramawar ziyartar Nnamdi Kanu, shugaban masu fafutukar kafa kasar Biyafara (IPOB) a tattaunawar da muka yi, ya bayyana cikin koshin lafiya da walwala, ya kuma kara tabbatar da juriyarsa duk da halin da yake ciki.

“Ya yi kira da a gudanar da zaben raba gardama, inda ya bayyana hakan a matsayin wani muhimmin mataki na cin gashin kansa, ya kuma kara jaddada imaninsa cewa bai aikata wani laifi ba face ya bukaci jama’ar mu su farka daga barcin da suke yi.

“Ya isar da saƙo mai ƙarfi na tabbatar da kai, lura da cewa yana shan magungunan da aka ba shi kuma ya ci gaba da kasancewa cikin koshin lafiya.

“Fiye da haka, ya nuna rashin jin dadinsa game da rashin shugabanci na gari a cikin al’ummar Igbo—wani sakaci da ya sa muryar jama’armu ta dushe a wani muhimmin lokaci.

“Kanu ya bayyana kwarin guiwa ga tawagar lauyoyin sa da kuma fatansa na sake shi a karshen watan Afrilun 2025.

Ezenekwe ya ce taron ya kasance wata muhimmiyar tunatarwa ga fafutukar ganin an amince da su, da adalci, da kuma ci gaban muradun Igbo a Najeriya.

Ya yi kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da ya ba da umarnin a saki Kanu, yana mai cewa yin hakan zai nuna cewa shugaban kasar ya jajirce wajen yin adalci.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp