Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP, ba ta aiki kuma nan ba da dadewa ba za wa’adin ta zai kare.
A cewar Ganduje, NNPP ta mutu kuma Rabiu Kwankwaso dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar a zaben 2023 yana son dawowa APC.
Tsohon gwamnan jihar Kano ya yi magana a ranar Talata a Abuja, lokacin da ya karbi tawagar Tinubu Support Group, TSG, a sakatariyar jam’iyyar.
Ya ce jam’iyya mai mulki za ta shirya tsaf domin tarbar Kwankwaso da hannu biyu-biyu.
Ya ce, “Jam’iyyar NNPP ta mutu, kuma nan ba da jimawa ba za a yi jana’izar ta, ina duba inda za mu binne gawar, an riga an gina akwatin gawar.
“Abin da ya rage a yanzu shi ne tono kabari, kuma tuni sun fara tono kabarin nan ba da dadewa ba.
“Ko da haka, wanda ake kira shugaban NNPP na kasa, shi ma ya ce bayan ya rasa kowa, yana so ya dawo wurinmu, za mu yi masa maraba, domin yana dawowa gida,” in ji shi.
A halin da ake ciki, Kwankwaso da NNPP sun sha musanta ikirarin sauya sheka da APC ke yi.
Da yake jawabi yayin taron majalisar zartarwa ta kasa NNPP a Abuja kwanan baya, Kwankwaso ya ce Ganduje ne zai hada shi a NNPP ba wai akasin haka ba.