fidelitybank

Nan ba da daɗe wa ba wa’adin NNPP zai ƙare – Ganduje

Date:

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP, ba ta aiki kuma nan ba da dadewa ba za wa’adin ta zai kare.

A cewar Ganduje, NNPP ta mutu kuma Rabiu Kwankwaso dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar a zaben 2023 yana son dawowa APC.

Tsohon gwamnan jihar Kano ya yi magana a ranar Talata a Abuja, lokacin da ya karbi tawagar Tinubu Support Group, TSG, a sakatariyar jam’iyyar.

Ya ce jam’iyya mai mulki za ta shirya tsaf domin tarbar Kwankwaso da hannu biyu-biyu.

Ya ce, “Jam’iyyar NNPP ta mutu, kuma nan ba da jimawa ba za a yi jana’izar ta, ina duba inda za mu binne gawar, an riga an gina akwatin gawar.

“Abin da ya rage a yanzu shi ne tono kabari, kuma tuni sun fara tono kabarin nan ba da dadewa ba.

“Ko da haka, wanda ake kira shugaban NNPP na kasa, shi ma ya ce bayan ya rasa kowa, yana so ya dawo wurinmu, za mu yi masa maraba, domin yana dawowa gida,” in ji shi.

A halin da ake ciki, Kwankwaso da NNPP sun sha musanta ikirarin sauya sheka da APC ke yi.

Da yake jawabi yayin taron majalisar zartarwa ta kasa NNPP a Abuja kwanan baya, Kwankwaso ya ce Ganduje ne zai hada shi a NNPP ba wai akasin haka ba.

 

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp