fidelitybank

Namibia sun zabi Mace ta farko a matsayin shugabar kasa

Date:

‘Yar takarar jam’iyya mai mulki a Namibia, Swapo, Netumbo Nandi-Ndaitwah, ta zama mace ta farko da aka zaɓa shugabar ƙasar a zaɓen makon da ya gabata wanda ake taƙaddama a kansa.

Hukumar zaɓen ƙasar ta ce Nandi-Ndaitwah mai shekara 72, ta samu sama da kashi 57 cikin ɗari na ƙuri’un da aka kaɗa inda ɗan takara mafi kusa da ita, Panduleni Itula ya samu kashi 26 cikin ɗari.

Nandi-Ndaitwah, wadda ita ce mataimakiyar shugaban ƙasar a yanzu, da wannan nasara za ta kasanace shugaba ta biyar kenan tun bayan da ƙasar ta yankin kudancin Afirka ta samu ‘yancin kai a 1990.

Kuma jam’iyyarta, Swapo, ita ce ke mulki tun daga samun ‘yancin har yanzu.

Sakamakon matsalolin da aka gamu da su na kayan aiki da kuma ƙarin kwana uku da aka yi a zaɓen a wasu sassan ƙasar, Itula ya yi zargin an yi maguɗi a zaɓen.

Yawancin jam’iyyun hamayya sun ƙaurace wa wajen bayyana sakamakon zaɓen a jiya Talata da daddare, a babban birnin ƙasar Windhoek.

Idan aka rantsar da ita za ta zama mace ta biyu kenan da ke shugabanci a Afirka, inda a yanzu ake da Samia Suluhu Hassan a Tanzania.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp