fidelitybank

Namibia sun zabi Mace ta farko a matsayin shugabar kasa

Date:

‘Yar takarar jam’iyya mai mulki a Namibia, Swapo, Netumbo Nandi-Ndaitwah, ta zama mace ta farko da aka zaɓa shugabar ƙasar a zaɓen makon da ya gabata wanda ake taƙaddama a kansa.

Hukumar zaɓen ƙasar ta ce Nandi-Ndaitwah mai shekara 72, ta samu sama da kashi 57 cikin ɗari na ƙuri’un da aka kaɗa inda ɗan takara mafi kusa da ita, Panduleni Itula ya samu kashi 26 cikin ɗari.

Nandi-Ndaitwah, wadda ita ce mataimakiyar shugaban ƙasar a yanzu, da wannan nasara za ta kasanace shugaba ta biyar kenan tun bayan da ƙasar ta yankin kudancin Afirka ta samu ‘yancin kai a 1990.

Kuma jam’iyyarta, Swapo, ita ce ke mulki tun daga samun ‘yancin har yanzu.

Sakamakon matsalolin da aka gamu da su na kayan aiki da kuma ƙarin kwana uku da aka yi a zaɓen a wasu sassan ƙasar, Itula ya yi zargin an yi maguɗi a zaɓen.

Yawancin jam’iyyun hamayya sun ƙaurace wa wajen bayyana sakamakon zaɓen a jiya Talata da daddare, a babban birnin ƙasar Windhoek.

Idan aka rantsar da ita za ta zama mace ta biyu kenan da ke shugabanci a Afirka, inda a yanzu ake da Samia Suluhu Hassan a Tanzania.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp