Hukumar Kula da Jiragen Sama ta kasa NAMA, ta tabbatar da harin da ‘yan ta’adda suka kai a filin jirgin sama na Kaduna a ranar Asabar.
Ta kuma bayyana sunayen jami’an tsaronta da ‘yan ta’addan suka kashe.
An bayyana shi da Shehu Na’Allah, wani jami’in tsaro da ke aiki a filin jirgin sama na Kaduna.
Manajan tashar jirgin, Misis Amina Salami, ta ce ‘yan bindigar sun mamaye filin jirgin ne ta shingen dajin da ke kusa da wajen da misalin karfe 1 na ranar Asabar, inda suka fara harbe-harbe ba da jimawa ba don tsorata ma’aikatan.