fidelitybank

Najeriya za ta shiga ƙungiyar BRICS – Brazil

Date:

Gwamnatin Brazil ta sanar da cewa Najeriya ta amince ta shiga cikin ƙungiyar ƙasashen duniya da ake yi wa laƙabi da BRICS.

Brazil, wadda ita ce ke shugabantar ƙungiyar a 2025, a cikin wata sanarwa, ta bayyana cewa Najeriya “ta ƙasance ƙasa da ke ƙara ƙarfafa hulɗar dangantaka tsakanin ƙasashen ɓarin kudancin duniya da kuma sauya salon shugabanci”, wanda abu ne da Brazil ke bai wa muhimmanci.

“A matsayinta ta ƙasa ta shida mafi yawan al’umma a duniya, kuma mafi yawan al’umma a Afirka, kuma ɗaya daga cikin ƙasashe mafiya ƙarfin tattalin arziƙi a Afirka, Najeriya na da kamanceceniyar manufofi da ƙasashen ƙungiyar,” kamar yadda sanarwar ta ma’aikatar harkokin waje ta Brazil ta sanar.

BRICS, ƙungiya ce ta ƙasashen da suka haɗa ba Brazil, Rasha, Indiya, China, Afirka ta kudu, Masar, Habasha, Indonesia, Iran da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa.

Ana wa ƙungiyar kallon kishiya ta ƙungiyar ƙasashe mafiya ƙarfin tattalin arziƙi ta duniya, wato G7.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp