fidelitybank

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Date:

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin kwashe ƴan ƙasarta da suka maƙale a ƙasashen Isra’ila da Iran, bayan tsanantar rikici tsakanin ƙasashen biyu.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a daren Talata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin waje, Kimiebi Ebienfa, ya ce jakadun Najeriya a Tel Aviv da Tehran na ci gaba da tuntuɓar ’yan ƙasar da rikicin ya rutsa da su, tare da aikin tabbatar da cewa an kwashe su cikin aminci da kariya.

Ma’aikatar ta buƙaci ’yan Najeriya da ke zaune a Isra’ila da Iran da su bi dukkan matakan tsaro da hukumomin ƙasashen suka shimfiɗa, sannan kuma su hanzarta tuntuɓar ofishin jakadancin Najeriya mafi kusa domin yin rajista da samun ƙarin shawarwari.

Ma’aikatar ta yaba wa jajircewar ofisoshin jakadancin Najeriya a Isra’ila da Iran wajen tuntuɓar ’yan ƙasar a wannan lokaci mai cike da ƙalubale, tare da jaddada cewa kariyar lafiyar ’yan Najeriya da ke kasashen waje na daga cikin manyan abubuwan da gwamnati ke bai wa muhimmanci.

“Ma’aikatar harkokin waje na sanar da cewa sakamakon rikicin da ke ƙara tsananta tsakanin Isra’ila da Iran, Gwamnatin tarayya na kammala shirye-shiryen kwashe ’yan Najeriya da ke cikin mawuyacin hali a ƙasashen biyu.” in ji sanarwar.

Sanarwar ta zo ne bayan hare-haren sama da Isra’ila ta kai a ranar Juma’a, inda ta hari wurare kimanin 100 a fadin Iran, ciki har da cibiyoyin nukiliya da na soji inda hare-haren suka hallaka manyan jami’an sojin Iran da dama.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp