Yanzu dai za a buga wasan sada zumuncin kasa da kasa tsakanin Super Eagles ta Najeriya da Albiceleste ta Argentina a kasar Amurka.
Za a yi wasan sada zumunci ne a ranar da ba a bayyana ba a watan Maris.
Tun da farko dai an shirya gudanar da wasan a China amma an soke shi ne sakamakon takaddamar da ta barke tsakanin fitaccen dan wasan Argentina Lionel Messi da hukumomin kwallon kafar China.
Messi dai ya fusata ‘yan kasar China ne bayan da ya ki buga wasan sada zumunci tsakanin kulob dinsa na Inter Miami da Hong Kong X1.
Dan wasan gaba yana fama da rauni a lokacin.
Argentina kuma za ta kara da El Salvador a wani wasan sada zumunci a watan Maris.
Super Eagles za ta yi amfani da wasan sada zumuncin ne domin tunkarar wasannin neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA a shekarar 2026 da Afirka ta Kudu da Jamhuriyar Benin a watan Yuni.