Kungiyar hadin gwiwa mai fafutukar ganin an gudanar da shugabanci nagari, JAGG, ta ce Najeriya na kan turbar farfadowa, idan har shugaba Bola Tinubu ya samu nasarar kawar da irin kudaden da ake barnatarwa wajen tafiya-tafiye.
Mataimakin shugaban kungiyar na kasa, Mista Abdulwaheed Odunuga ne ya bayyana hakan a wata hira da manema labarai a ranar Laraba a Legas.
Yana mai da martani ne kan umarnin shugaban kasar nan ya yanke adadin jami’an da za su raka shi da sauran manyan jami’an gwamnati a duk wata tafiya ta kasashen waje.
Ya ce ’yan Najeriya sun sha wahala sosai saboda dimbin almubazzaranci a harkokin mulki da kuma a tsakanin masu rike da mukaman gwamnati.
“Abin farin ciki ne kuma za mu so mu yaba wa shugaban kasa kan wannan mataki.
“A wajenmu, ba wai yana rage kudin gwamnati ba ne, sai dai yana rage almubazzaranci, kuma bai kamata a takaita tafiye-tafiye zuwa kasashen waje kadai ba.
“Idan shugaban kasa zai iya rage wadannan sharar gida ina da kwarin gwiwar cewa ba za mu bukaci lamuni don samar da kasafin kudin ba,” in ji Odunuga.
Yayin da yake bayyana matakin a matsayin mai mahimmi kuma abin lura, Odunuga ya ce an yi shi ne da nufin rage kashe kudaden da ake kashewa a kan takardun shaida da alawus-alawus.