fidelitybank

Najeriya za ta dawo ragamar ta idan Tinubu ya daure a kan gyara – JAGG

Date:

Kungiyar hadin gwiwa mai fafutukar ganin an gudanar da shugabanci nagari, JAGG, ta ce Najeriya na kan turbar farfadowa, idan har shugaba Bola Tinubu ya samu nasarar kawar da irin kudaden da ake barnatarwa wajen tafiya-tafiye.

Mataimakin shugaban kungiyar na kasa, Mista Abdulwaheed Odunuga ne ya bayyana hakan a wata hira da manema labarai a ranar Laraba a Legas.

Yana mai da martani ne kan umarnin shugaban kasar nan ya yanke adadin jami’an da za su raka shi da sauran manyan jami’an gwamnati a duk wata tafiya ta kasashen waje.

Ya ce ’yan Najeriya sun sha wahala sosai saboda dimbin almubazzaranci a harkokin mulki da kuma a tsakanin masu rike da mukaman gwamnati.

“Abin farin ciki ne kuma za mu so mu yaba wa shugaban kasa kan wannan mataki.

“A wajenmu, ba wai yana rage kudin gwamnati ba ne, sai dai yana rage almubazzaranci, kuma bai kamata a takaita tafiye-tafiye zuwa kasashen waje kadai ba.

“Idan shugaban kasa zai iya rage wadannan sharar gida ina da kwarin gwiwar cewa ba za mu bukaci lamuni don samar da kasafin kudin ba,” in ji Odunuga.

Yayin da yake bayyana matakin a matsayin mai mahimmi kuma abin lura, Odunuga ya ce an yi shi ne da nufin rage kashe kudaden da ake kashewa a kan takardun shaida da alawus-alawus.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp