fidelitybank

Najeriya za ta ciyo bashin dala biliyan 2.2 a bankin duniya – Wale Edun

Date:

Gwamnatin tarayya na sa ran karɓar rancen dala biliyan 2.2 daga bankin duniya da kuma wani tallafin daga bankin raya ƙasashen Afirka, AfDB.

Ministan kuɗi, Wale Edun ne ya bayyana haka yayin wani taron manema labarai na haɗin gwiwa a ƙarshen tarukan bankin duniya da IMF a birnin Washington DC da ke Amurka.

Da yake magana kan hanyoyin samun kuɗaɗe don tallafa wa tattalin arzikin Najeriya, Edun ya lissafa kuɗaɗen da ƴan Najeriya mazauna ƙetare ke tura wa ƙasar da hannun jari da cibiyoyin bankin duniya da sauran ƙungiyoyin samar da ci gaba na ƙasashen duniya.

Ya ƙara da cewa Najeriya za ta kuma amfana daga tallafin kasafin kuɗi da yake da kuɗin ruwa ƙalilan daga bankin raya ƙasashen Afirka inda ya ce ana tattaunawa da ƴan ƙasashen waje masu zuba hannun jari.

Edun ya bayyana cewa kuɗin da ake samu daga man fetur ne babbar hanyar samun kuɗin shiga ga Najeriya sannan ƙudirin shugaban Najeriya Bola Tinubu na ƙara samar da ɗanyen mai daga ganga miliyan 1.6 duk rana zuwa ganga miliyan biyu kowace rana.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...
X whatsapp