fidelitybank

Najeriya ta yi nasara a kotun Birtaniya bayan an nemi ta biya diyyar dala biliyan 11

Date:

Najeriya ta yi nasara a karar da ta daukaka kan wani hukunci da ke neman ta biya diyyar dala biliyan 11 ga wani kamfanin kasashen waje bayan rushewar wata kwangilar shimfida bututun iskar gas.

Kamfani P&ID mai hedikwata a Virgin Islands na Birtaniya ne ya kai Nijeriya kara a kotun sasanta rikicin kasuwanci, inda ya nemi diyyar kudin da suka kai kashi daya cikin uku na asusun ajiyar kasashen wajen kasar.

Mai shari’a Robin Knowles ya karbi bahasin kalubalantar hukuncin farko da Najeriya ta yi a wani hukunci da ya gabatar ranar Litinin.

“Ban amince da dukkan zarge-zargen da Najeriya ta yi ba,” alkalin ya fada a hukuncin da ya yanke. Sai dai ya kara da cewa hukuncin kotun sasanta rikicin kasuwanci “an same shi ne ta hanyar damfara kuma hanyar da aka same shi, ya saba da manufar aikin gwamnati”.

A shekara ta 2010 ne, Najeriya ta bai wa kamfanin Process & Industrial Developments (P&ID) kwangilar aikin ginawa da gudanar da wata tashar sarrafa iskar gas tsawon shekara 20 a kudancin najeriya, a wani bangare na wani babban shirin hako dumbin arzikin iskar gas da Allah ya hore wa kasar.

Sai dai bayan rushewar yarjejeniyar, kamfanin P&ID ya garzaya gaban kotun sasanta rikice-rikicen kasuwanci da ke London a 2017, wadda ta yanke hukuncin cewa Najeriya ba ta gaskiya kuma ta biya kamfanin dala biliyan 6.6 na asarar da ya yi.

Kudin dai ya yi ta karuwa har zuwa sama da dala biliyan 11 saboda kudin ruwa.

Kiyasi na cewa kudin ya ninka har sau 10 a kan kasafin kudin Najeriya na fannin lafiya na 2019.

Lauyoyin Najeriya sun ce kasar ta tsinci kanta ne a cikin “wata makarkashiyar cin hanci da damfara” daga kamfanin P&ID, wanda suka ce ya bayar da toshiyar baki ga manyan jami’an gwamnati don samun kwangila, daga nan kuma sai ya rika bayar da rashawa ga lauyoyin kasar don samun takardun sirri na hukuma a lokacin shari’ar.

P&ID ya musanta cewa ya samu kwangilar ne ta hanyar ba da toshiyar baki ko ya rika bayar da cin hanci ga lauyoyin Najeriya a lokacin sauraron shari’ar, inda ya dora alhakin rushewar yarjejeniyar iskar gas din a kan rashin kwarewar cibiyoyin gwamnati da ke da alhakin tafiyar da shari’ar.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp