fidelitybank

Najeriya ta yi asarar Naira Tiriliyan 2.9 a harƙallar kwangiloli – EFCC

Date:

Sabon shugaban Hukumar Yaki da cin Hanci da Rashawa ta (EFCC), Ola Olukoyede, ya ce an yi asarar naira tiriliyan 2.9 ta hanyar rashin gaskiya a harkar kwangiloli da zamba wajen sayan kayayyakin gwamnati a tsakanin shekarar 2018 zuwa 2020.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa Olukoyede ya bayyana hakan ne a lokacin da yake amsa tambayoyi daga Sanatoci a yayin tantance shi domin tabbatar da shi a matsayin sabon shugaban hukumar EFCC ranar Laraba.

Ya ce adadin kuɗin ya isa a biya kuɗin gina tituna na aƙalla kilomita 1,000, da gina manyan makarantu kusan 200, da kuma ilimantar da yara kusan 6,000 daga matakin firamare har zuwa jami’a a kan Naira miliyan 16 ga kowane yaro.

Da yake ƙarin haske game da hurumin binciken hukumar, Olukoyede – da Majalisar Dattawan ta tabbatar bayan tantancewar – ya bayyana cewa a matsayinsa na shugaban EFCC yana da ‘yancin gudanar da bincike ga kowa a ƙasar.

Ya kuma yi alƙawarin rashin saɓa ƙa’ida a gudanar da aikinsa, yayin da ya sha alwashin yin aiki da al’ummar Najeriya tare da tabbatar da gaskiya da kuma ɗaukar matakan kariya don rage ƙararrakin da aka daɗe ana yi.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp