fidelitybank

Najeriya ta nema ƙarin tallafin MDD kan ambaliyar Maiduguri

Date:

Mataimakin shugaban ƙasar Najeriya Kashim Shettima ya gana da Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya António Guterres a shalkwatarta da ke birnin New York na Amurka.

Cikin wani saƙo da kakakin Majalisar Dinkin Duniya ya wallafa a shafinsa na X, ya ce a lokacin ganawar an tattauna batutuwa da dama da suka shafi tsaro da ayyukan jin ƙai da tattalin arziki da sauransu.

Shettima wanda yake wakiltar Shugaba Bola Tinubu a babban taron Majalisar Dinkin Duniyar karo na 79 ya kuma zanta da mataimakiyar Sakatare-Janar ta majalisar, Amina Mohammed.

Mataimakin shugaban ƙasar ya kuma buƙaci ƙarin tallafi domin magance matsalolin da sauyin yanayi suke janyowa, inda ya nanata buƙatar ƙarin tallafi ga mutanen da ambaliya ta illata a jihar Borno.

A nasa ɓangaren, Mista Guterres ya jajanta wa Najeriya, sannan ya yi alƙawarin samar da ƙarin tallafin.

Ya ce Majalisar Dinkin Duniya za ta cigaba da tallafa wa Najeriya, sannan ya jinjina wa shugaba Tinubu, inda ya ce Najeriya ƙawar arziki ce ga Majalisar.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp