Sakamakon satar danyen man fetur, Najeriya ta yi asarar dala biliyan 1 na kudaden shiga a cikin rubu’in farko na shekarar 2022, lamarin da ke barazana ga tattalin arzikin kasar da ke kan gaba a nahiyar Afirka.
Gbenga Komolafe, shugaban hukumar kula da harkokin man fetur ta Najeriya ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da kamfanin dillancin labarai na Reuters.
Najeriya dai na asarar miliyoyin ganga na danyen mai a duk shekara, sakamakon sata da barna, ciki har da satar danyen mai daga bututun mai da manyan kamfanonin mai ke gudanarwa. Wannan ya nuna yadda rashin tsaro ke haifar da babbar asarar kuÉ—i ga al’umma.