fidelitybank

Najeriya ta musanta gaza biyan bashin China

Date:

Ofishin kula da basussuka na ƙasa, ya musanta zargin cewa gwamnatin tarayya ta gaza biyan kuɗin ruwa ga China don samun bashi.

Kafofin yaɗa labarai sun ruwaito cewa an ci tarar Najeriya $90m bayan bashin da China ke bin ta ya ƙaru zuwa dala miliyan 240 a cikin shekaru biyu da suka gabata.

An ce an karɓo bashin ne domin gyara wasu layukan dogo a ƙasar.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba, DMO ya musanta rahotannin, inda ya ce Najeriya ta jajirce wajen ganin ta mutunta bashin da ake bin ta, kuma ba ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen biyan basussukan da ta ciyo.

Sanarwar ta kara da cewa, “Najeriya na ci gaba da jajircewa wajen ganin ta biya bashin da ake bin ta a kan lokaci.”

Don haka ofishin ya bukaci jama’a da su yi watsi da rahotannin.

Ya zuwa watan Disamba na 2021, DMO ya ce, bashin da China ke bin Najeriya ya kai dala biliyan 4.1, sai dai bai yi ƙarin haske ba kan yawan bashin da Najeriya ta ciyo ba daga ƙasar China ba zuwa yanzu.

A shekarun baya-bayan nan dai Najeriya ta yi asarar kuɗin shiga sakamakon yawaitar hare-haren da ake kai wa kan hanyoyin jiragen kasa da kuma sace fasinjojin da ya yi sanadiyar dakatar da zirga-zirgar jiragen ƙasa a wasu hanyoyin na ɗan wani lokaci.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp