Gwamnatin Tarayya ta lalata tarin hauren giwa mai ƙimar tsabar kuɗi har dala miliyan 11 da ta ƙwace daya hannun masu fasa-ƙwauri.
An dai yi fasaƙwaurin hauren ne daga ƙasashen Afirka masu dama.
Ministan Muhalli na Najeriyar, Iziaq Adekunle Salako wanda ya shaida hakan yayin wani taro a Abuja, ya ce ya ɗauki matakin lalata tarun hauren giwar ne domin aikewa da saƙo da ke nuna rashin amincewarsu ga irin wannan aiki.
Ko a watan Oktoba ma sai da aka lalata tan-tan na ɗan kunya da aka ƙwace daga hannun masu simoga.
Masana sun ce ana kashe dubban ɗaruruwan giwaye a kowace shekara domin yin safarar haurensu, duk da haramcin cinikayyarsu da duniya ta yi shekaru da suka gabata.
Masu kare dabbobi sun ce Najeriya ta zamo a gaba-gaba wajen safarar sassan dabbobi.