Tsohon gwamnan Kaduna kuma jigo a jam’iyyar Social Democratic Party, SDP, Nasir El-Rufai, ya ce, Najeriya ta koma baya tun bayan hawan shugaba Bola Tinubu.
El-Rufai ya zargi gwamnatin Tinubu da rashin iya aiki, son zuciya da cin amanar manufofin kafa jam’iyyar All Progressives Congress, APC.
Ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da Deutsche Welle Hausa a Katsina.
Ya ce a yau Najeriya ta fi tabarbarewar tsaro da tattalin arziki da shugabanci fiye da yadda ta kasance a gwamnatocin baya.
“Tun lokacin da Tinubu ya hau kujerar shugabancin Najeriya, kasar ta fara komawa baya.
“Rashin tsaro ya karu, tattalin arzikin kasar yana raguwa, mawadata sun zama matalauta, kuma batun kabilanci yana karuwa.
“Duk wanda zai ba wa wani mukami to ya zama wanda ya sani ko kuma daga kabilarsa.
“Za su iya watsi da hakan, amma ‘yan Najeriya ba wawaye ba ne, babu yadda za a yi sunanka ya zama haka, kuma za su ce a’a, kai dan Katsina ne,” in ji shi.