fidelitybank

Najeriya ta gaza wajen kare rayuka da dukiyar al’umma – AMNESTY

Date:

Ƙungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta zargi gwamnatin Najeriya da gazawa wajen kare rayuka da dukiyar al’ummar ƙasar lamarin da ya sanya masu aikata laifi ke kai farmaki tare da hallaka al’umma.

Ƙungiyar ta bayyana haka ne a matsayin martani kan rahotanni kai hare-hare a jihar Zamfara, inda aka hallaka “mutane kimanin 20”.

A tattaunawarsa da BBC, shugaban ƙungiyar Amnesty International a Najeriya, Isa Sanusi ya yi zargin cewa akwai nakasu a dabarun da Najeriyar ke amfani da su wajen yaƙi da matsalar tsaro a ƙasar.

“Dabarun da gwamnati ke amfani da su wajen kare mutane na da rauni, kuma ya kamata a sake dabara,” in ji Sanusi.

Ya kuma yi zargin cewa a yanzu ƴan siyasar ƙasar sun mayar da hankali ne wajen tunkarar zaɓen shekara ta 2027 a maimakon kare rayuwar al’umma.

“Abin da ƴan siyasa suka mayar da hankali a kai shi ne ya za mu ci zaɓe?”

Ya ƙara da cewa ya kamata gwamnati ta fifita kyautata rayuwar mutane a maimakon siyasa.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp