Ɗan wasan Najeriya, Zaidu Sanusi ya ce babu wata tawagar da ta fi Super Eagles ƙarfi a Gasar AFCON, bayan da Najeriya ta samu damar zuwa zagaye na biyu na gasar ta bana.
A jiya ne Najeriya ta doke Guinea-Bissau da ci ɗaya mai ban haushi, a nasarar da ta bai wa tawagar ƴan ƙwallon Najeriya damar tsallakewa zuwa zagaye na gaba.
Sai dai a cikin wasa uku Najeriya ƙwallo uku kacal ta iya zurawa a ragar abokan hamayyarta.
A zagaye na gaba Najeriyar za ta kara ne da duk ƙasar da ta zo ta biyu a Rukunin C, wato rukunin da ya ƙunshi Senegal, Kamaru, Gambia da Guinea.