Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama na kasa, ya fara gudanar da bincike kan zargin cin zarafin fasinjoji sama da 200 da suka nufi Najeriya a jiragen sama na Lufthansa na ƙasafarr Jamus.
Kafofin yaɗa labaran sun ce jirgin ya yi barazanar kiran ‘yan sanda a ranar Juma’ar da ta gabata bayan fasinjojin da jirgin ya ɗauka suka bukaci a samar musu da wurin zama bayan jinkirta tashinsu.
Rahotanni sun bayyana cewa jirgin da ya fito daga Frankfurt zuwa Legas, da aka tsara zai sauka a filin jirgin sama na Murtala Muhammed, amma sai da ya yada zangon a Cotonou a ƙasar Benin da Malabo na ƙasar Equatorial Guinea.
Kamfanin Lufthansa ya nemi afuwar jinkirin da jirgin ya samu a wata wasika da ya aike wa fasinjojinsa a ranar Juma’ar da ta gabata.
Fasinjojin sun yi zargin cewa ba a rufe filin jirgin sama na Legas ba, saɓanin iƙirarin da matukin jirgin na Lufthansa ya yi.
Sam Adurogboye, jami’in hulɗa da jama’a na NCAA, a ranar Alhamis ya ce hukumar ta fara gudanar da bincike kan lamarin bayan samun koke-koke daga fasinjojin. BBC ta tuntubi kamfanin jirgin domin jin karin bayani.