fidelitybank

Najeriya ta fara binciken jirgin Jamus a kan cin zarafi

Date:

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama na kasa, ya fara gudanar da bincike kan zargin cin zarafin fasinjoji sama da 200 da suka nufi Najeriya a jiragen sama na Lufthansa na ƙasafarr Jamus.

Kafofin yaɗa labaran sun ce jirgin ya yi barazanar kiran ‘yan sanda a ranar Juma’ar da ta gabata bayan fasinjojin da jirgin ya ɗauka suka bukaci a samar musu da wurin zama bayan jinkirta tashinsu.

Rahotanni sun bayyana cewa jirgin da ya fito daga Frankfurt zuwa Legas, da aka tsara zai sauka a filin jirgin sama na Murtala Muhammed, amma sai da ya yada zangon a Cotonou a ƙasar Benin da Malabo na ƙasar Equatorial Guinea.

Kamfanin Lufthansa ya nemi afuwar jinkirin da jirgin ya samu a wata wasika da ya aike wa fasinjojinsa a ranar Juma’ar da ta gabata.

Fasinjojin sun yi zargin cewa ba a rufe filin jirgin sama na Legas ba, saɓanin iƙirarin da matukin jirgin na Lufthansa ya yi.

Sam Adurogboye, jami’in hulɗa da jama’a na NCAA, a ranar Alhamis ya ce hukumar ta fara gudanar da bincike kan lamarin bayan samun koke-koke daga fasinjojin. BBC ta tuntubi kamfanin jirgin domin jin karin bayani.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp