Kungiyar kwallon kafar Najeriya, Super Eagles, ta zura kwallonta ta farko a ragar Masar a wasan da suke yi a gasar cin kofin nahiyar Afirka.
A dai-dai minti na 30 da take wasan ne Kelechi Iheanacho ne ya zura kwallon.
Yanzu haka Super Eagles ta sami maki uku a kan kasar Masar, inda ta zama na daya a cikin rukunin, yayin da kasar Masar ta koma mataki na karshe.
a ranar Asabar ne Najeriya za ta kara wasan ta na biyu da kasar Sudan da karfe biyar na yamma, ranar Laraba 19 ga wata za ta yi wasa na uku da Guinea Bisau.