fidelitybank

Najeriya ta dage da yin ciniki da Naira maimakon kudin China – Falana

Date:

Wani babban Lauyan Najeriya Femi Falana, ya yi kira ga ‘yan kasuwa su dage wajen yin hada-hadar kasuwanci da Naira, ciki har da amfani da ita wajen biyan kuɗin kayan da ake shiga da su ƙasar daga China.

Tashar talbijin ta Channels ta ambato Falana na tunasar da ‘yan Najeriya game da yadda gwamnatin ƙasar da China suka ƙulla yarjejeniyar musayar kuɗi shekara biyar da ta gabata.

Ya yi nuni da cewa, cinikin wanda ya kai RMB biliyan 16 ko kuma Naira biliyan 720, an yi shi ne don samar da isassun kuɗaɗen gida ga masu masana’antu na Najeriya da China da sauran ‘yan kasuwa, tare da rage matsalolin da ake fuskanta wajen neman dalar Amurka.

An kuma tsara musaya tsakanin ƙasashen biyu don inganta sauri da sauƙaƙawa, da yawan hada-hadar kasuwanci tsakanin ƙasashen biyu.

Lauyan ya ƙara da cewa, duk da tabbatar da cewa yarjejeniyar har yanzu tana nan daram kuma tana aiki, amma har yanzu babban bankin Najeriya bai bar ‘yan ƙasar su yi kasuwanci a kasar China ta hanyar amfani da naira ba.

Lamarin da ya ce ya zama dole, inda ya bukaci ‘yan kasuwar Nijeriya su dage su rika hada-hadar kasuwanci da naira, ciki har da biyan kuɗin kayan da ake shiga da su daga kasar China.

legit nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp