fidelitybank

Najeriya ta buƙaci kamfanin Binance ya biya ta diyyar dala biliyan 10

Date:

Gwamnatin Najeriya ta buƙaci shafin musayar kuɗin intanet na Binance ya biya ta kuɗi dalar Amurka biliyan 10 a matsayin tara, bisa iƙirarin da gwamnatin ta yi na asarar da ta tafka sanadiyyar ayyukan shafin.

Gwamnatin ta zargi shafin na Binance da zuzuta farashin musayar kuɗaden waje ta hanyar yin hasashe maras tushe da kuma shaci-faɗin darajar naira, lamarin da ya sa darajar naira ta zube da kimanin kashi 70 cikin 100.

A ranar Alhamis ne gwamnatin Najeriya ta tabbatar da cewa tana tsare da wasu manyan jami’an shafin Binance biyu, waɗanda jami’an tsaro ke yi wa tambayoyi bisa zargin shafin da zama wata kafa ta halasta kuɗaɗen haram da kuma samar da kuɗi ga ƴan ta’adda.

Wannan ya biyo bayan iƙirarin da Babban Bankin Najeriya ya yi a ranar Talata cewa kuɗi kimanin dala biliyan 26 ne aka yi safarar su ta shafin Binance daga Najeriya zuwa wasu wuraren da ba a sani ba.

Bayo Onanuga, wanda shi ne mai magana da yawun shugaban Najeriya ya shaida wa BBC cewa: “Jami’an na Binance na bai wa gwamnati haɗin kai ta hanyar samar da bayanai”.

Har yanzu dai Binance bai ce komai ba game da batun tsare jami’an nasa biyu a Najeriya.

Babban Bankin Najeriya na shan matsi wajen ganin ya daidaita darajar naira wadda farashinta ke ci gaba da tangal-tangal.

Faɗuwar darajar naira ta ƙara damalmala halin tsadar rayuwa da al’ummar Najeriya ke ciki sanadiyyar tashin farashin kayan masarufi da na abinci da sufuri, wanda ya haifar da jerin zanga-zanga a wasu yankunan ƙasar.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp